ALIYU GADANGA..!

Background color
Font
Font size
Line height

*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_

*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_

*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*

_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_

*Intelligent Writers Association*✏

_* Oh ni Jikar Fati😿Gabadaya yau ba"a barni nayi barcin Safe ba,gabadaya Anki barina nayi Sukuni ko"ina naje GADANGA..GADANGA...Toh gashinan Dai kada asamu masu cinyeni danya ban gasu ba😂 Nasan in ban sakoshiba,Akwai masu zuwa har zaria sucini Tara,irinsu TEAM AZEEMAR GADANGA😘Happy Lahadi day😂😜Asha karatu lafiya Masoyan kwarai*_💞💖

   *Chapter 30..*

    ""Gimbiya Fasilatu ta kira likitan mai martaba Tasanar dashi ko mintigoma  baiyi ba, ya iso masauratar,kai tsaye akayi mishi iso shashen maimartaba,koda ya isa ya iske maimartaba nata sambatu yana kiran Sunan Suwaiba,bai bata lokaci ba ya nemi da su Ummah su bashi wajen don yasamu damar gudanar da aikinshi,suna Fita ya karisa gamai maimartaba wanda ke zaune yayi Tagumi yana Ta so kwalkwalwarsa Ta tunamai Sauran Abubuwa ammh Abu yaci Tura,Likitan baiyi mgana ba,illah bude akwatin kayan aikinsa ya Fito da allurai ya harda harda ya juye a Siriji yayi mai martaba ita,wanda ko minti biyar bai karaba ya sulale yana barci,koda likitan ya Fito baice masu Ummah komai ba,illah sanar dasu dayayi"Da zaran ya Farka zai Dawo daidai Ranki Shi dade.."Sallama sukayi yatafi wanda dama Likitan Shima zuru"ar Mairtaba tsohon sarki ne,da yake ga Sarki Abdulnasser din.

Har garin Allah yawaye maimartaba Bai Farka ba,yana ta barcinsa Hankalinsa kwance,Tuni lbrin ya ishi kunnen sauran iyalansa da kuma Shamaki tare da waziri da galadima,su suka sanar da Fada  cewa sarki bazai samu zama ba yau sakamakon baitashi da jin dadin jikinsa,Fatan samun sauki akayimai sai Waziri ya Karbi sarki Aranar aka cigaba da gudanar da Mulkin.

   *********************

Suna Shiga cikin gidan Aliyu,suka zazzauna,Aliyu bakinsa yaki Rufuwa saboda murna wayarsa yazaro yana Fadin"Dude ni nama Rasa wazan Fara kira goggo ko kawu? yafada yana Danna wayar dariya Jabir yayi kafin yace"kira kawu first shine ke kusa goggo kuma,in son samu ne ayimata Big Suprise kawai..."Dariya sukayi gabadaya.

Umar yace"Nikuma sai komai ya kammallah zan kira video call na hadaka da maimartaba nagani ko yaya zaiyi..? Shuru Aliyu yayi yana mirmishi daidai lokacin da Kawu ya daga kiransa yana Fadin"Aliyu Gadanga ya"akayi ne? Bakinsa duka abude yace"Kawu yau Allah ya gwadamin dan"uwa na,kawu yau  naji lbrin dangina,Ashe nima Da"ne kamar kowa ina da uba da yan"uwa da kanne da yayye.."Yafada idonsa na cikowa Da kwallah.

Kawu Bala dake zaune a office yayi Saurin mikewa yana Fadin"Aliyu are u Serious....? Da hanzari yace"Wlh kuwa kawu kazo barrak dinmu yanzu kaga wani Abun mamaki.."Kawu bai jira cewarsa ba ya datse kiran,alokacin yana da tattaunawa da yan jaridu,ammh ya tsallake Shida tawaganshi Suka Shisshiga mota sai bariki,tun amota yake addu"a Allah yasa Abunda Aliyu yafadamai da gaskene.

Aliyu najin karar Jiniyar motocin Kawu ya Fito da gudu,baima jira yakai ga Fitowa ba ya bude mota ya Riko hannunsa yana fadin",Taho kawu kaga wani abu.."Yafada yana Jansa zuwa cikin gidan,da hanzari ya Bishi yana kara saba babbar rigarsa Suna shiga cikin Falon kawu yaci karo da Umar zaune yana mai mirmishi Zaro ido kawu yayi yana bin Umar din da kallo,Kafin kuma yakoma yana bin Aliyun da kallo,Kawu yayi tsaye kafin ya Durkushe kasa kawai yana Fadin"Sarki ya tabbata ga Allah Shugaban kowa da kowa.."Yafada yana kai goshinshi kasa yadade kafin ya dago,koda yadago hawaye ne sharkaf bisa Fuskarsa,Aliyu ne yadagosa yana Fadin"Kaima kayi kuka ko kawu,wlh nima nayi,banta zaton zan yi Farinciki irin na yau ba,kawu kaga kamana dashi ko,kuma muna using da Surname iri daya His Name is Umar Abdulnaseer Tambari buzu..."Hannunsa Kawu ya riko ya karisa ga Umar yariko hannunsa ya hada dana gadanga yana Fadin"Ka sanar dani wani Abu game da mahaifinku Shin Abdulnaseer na raye acikin Duniyar nan"?Mikewa Umar yayi yana Fadin"Tabbas Maimartaba na Raye,ammh kuma yana rayuwa da mafarkin dakuma damuwarku,koda da darana daya Abbah bai taba Fidda rai da Allah zai bayyanamai Sirrin boye ba.."Ido Kawu ya zaro yana Fadin"Naji kace maimartaba kuma? dariya Umar yayi kafin yace"Eh Shine Sarkin dake mulkan *MASARAUTAR TAMBARI BUZU DAKE YANKIN AGADEZ..* Baya kawu yaja yana Fadin"Allah mai hikima da kari,babu wanda ke tsarawa kuma ya zartar lokaci daya sai Ubangiji.."Ya fada yana jinjina kai,kafin ya zauna sukoma suka sakashi atsakiya Kawu ya kalli Umar yace"Kabani wani lbri game da Abdulnaseer...'Nan Fa Umar ya basu lbrin Abunda ya sani game da mafarkin da maimartaba keyi,dakuma fadamai dayayi yayi Rayuwa A nageria ammh bazai iya Tuna awani gari bane,ako awani yanki bane,Shidai lokacin da Hankalinsa ya dawo ya Tsinci kansa ne awani gari,ammh kuma har mutumin daya taimakamai ya kawoshi har masarautarsu bai fadamai awani gari bane alokacin,ammh kullum cikin mafarkin wata mata da Danta yake,suna ahalin neman Taimakonsa..."

  jinjina kai kawu ketayi yana fadin"Kaji hikimar ubangiji ko Aliyu,Ai bakowa Allah ke Nunamai ba Sai Suwaiba dakai,Allah mai hikima" Kawu ke Fada Haryanzu yana mamakin al"amarin Jabir Shima na gefe yana Jin Abun kamar amafarki,Umar yasaka hannu a aljihu ya zaro wayarsa yana Fadin"Bari na kira waya zuwa gida.."Aliyu ya mike da hanzari yana Fadin"Kawu zan Sanar da goggo.."Rikosa kawu yayi yana Fadin"kyaleta ba yanzu ba,kasan Suwaiba bata iya Rudewa ba,kabari mufara ganin Abdulnaseer din mugani ko zai Shaidamu..."Yafada daidai Lokacin Zafira ta daga kiran Umar hoton ta ya bayyana Tana Fadin"La yaya Soja sai yau zaka Tuna damu ko,Safaratu taho ga yaya Soja ya kiramu daga Nageria.."Da gudu ko tataho tana Murna tana Fadin!"La yaya Sojan mutan Nageria,take fada daidai lokacin da hotonta ya bayyana Yanmatane,daya nada Shekara sha takwas daya kuma nada Sha biyar,Dukkansu kammansu daya Sai dai su suna da dan jiki,ammh yadda kaga Umar haka suke,Sai dai su yanayin idonsu da karan hancinsu yafi iri daya dana Ali zaki

Mirmishi yayi musu yana Fadin"Aiki ne yamana yawa Shiyasa ban kiraku ba,ya gida,ina ummah mai babban daki,kucemata nayi kewarta ina mommy nayi ta kiran wayarta bata daga ba..",Bata Fuska sukayi suna kallon Juna ganin haka sai hankalinsa ya tashi ya mike yana tambayansu"Lafiya meyafaru kowani Abu yasamu mommyne?Saurin dakatar dashi sukayi Suna Fadin"A"a yaya dama Abbah ne fa..."Afusace yace!Me Abban yayi me..? ganin yadda ya daka musu Tsawa ne yasa Zafira tayi Saurin cewa"Bafa wani Abu bane yaya Dama Abbah ne Tun Shekaran jiya bayi da lafiya,su mommy ma dasu Ummah chan Shashensa suke wuni.."Kai ya dafe yana ambatom Sunan Allah,su kawu dasuka koma gefe sukayi Tsuru suna binsa da kallon mamaki,Aliyu kuwa kamar ya warce wayar yaga Yaran dake mgana domin Sosai muryansu ke saukarmai da wani Farinciki,ammh jin Sun Ce Abbah bai da lafiya sai da yaji Faduwar gaba

Da hanzari Umar yace"Ku tashi maza ku Isa Shashen Abbah yanzu ku hadani da mommy"Dako hanzari kowacce ta mike dama suna sanye duka da alkyyabansu suka Fice suna ta mai Surutu,suna bashi lbrin ciwon Abbah ammh shiko jinsu bayayi burinshi su isa su mikama Mommy wayar,suna isa barayin na maimartaba suka isake Gimbiya Fasilatu da mahaifiyarsu gimbiya Razeenah sai Ummah mai babban daki wato kakarsu kenan wacce ta haifi maimartaba Suna zaune bisa Wani lafiyayyen Cafet,kowacce taci alkayabba takame,Ummah ce kadai ta sanya wani katon lullube,sai maimartaba dake kwance kan gadonsa idonsa biyu,kansa na bisa cinyar Ummah mai babban daki,suna Shiga suka isa ga Gimbiya Fasilatu sukace"Mommy ga waya yaya Soja nasan mgana dake.."Sukace suna mika mata wayar,Amsa tayi tana Fadin"Allah yasa baku Fadamai ba..? baki Zafira ta tura tana Fadin",Tambayanmu yayi muka Fadamai gaskiya."hararansu Tayi kafin ta maida hankalinta ga wayar inda taga hoton danta ya bayyana mirmishi tayi tana Fadin"Yarima mazan Fama.."Gimbiya Razeenah dake gefe ta yamutsa Fuska ta kauda kai.

Umar ya Shafa kanshi yana Fadin!"Mommy meyafaru da Abbah ne...? Dan muskutawa tayi Tana Fadin"Wlh bawani abun tada hankali bane Umar,kawai mafarkin daya sabayi ne tun Shekara jiya ya Farka yana ta kiran wani Suna,yana fadin wai matarsa ne,ammh ya manta awani gari take wai sanda ya bar gida ,a inda yajene ya aureta,kuma yafadi wajen,yakasa Shine fa Tun Ranar jiki yaki dadi,yakasa daina sakama kansa damuwa gashi har jininsa ya hau,baka Tunanin kawai Kwakwalrsane Bata samun hutu...!Tunda Tafara mgana Umar ya kafeta da ido,yayinda Aliyu yaji jinin jikinsa ya daskare,shiko kawu baki kadai ya rike yana kara tabbatar da ikon Allah.

Bakin Umar na Rawa yace"Wa...Wani Suna yake kira Mommy.."Tabe baki Tayi kafin tace"Ko Saddiqa ko wama,kamar dai *SUWAIBA* ko..? tafada tana kallon gimbiya Razeenah wacce ke kallonta ta wutsiyar ido,banza da ita tayi,don ita akwaita da iko ne wani lokacin,jin Sunan da Tafada yasa Umar Saurin Fadin"Mommy ku tada Abbah ku basa wayar wlh Allah ne ya Turoni nan don na cikema Abbah ragowan Abun da ya Shigemai Duhu,ku basa wayar na gano wadanda yake nema.."Dayake video cll ne,kowa naji,ai maimartaba dake kwance kan ciyar Ummah sai gashi ya mike kan kafafunsa ya diro daga kan gado,kafin ma Gimbiya Fasilatu tayi wani Abu ya Fizge wayar Fuskarsa ta bayyana yana kallon Umar yace"da gaske...Da gaske Umarun Faruqu ka ganinmin Suwaibata..? yafada cikin muryan dattako ammh ta Shake saboda damuwa.

Umar dake kallon mahaifinsa yaji hawaye sun kawomai,kai ya dagamai yana saka hannu ya yafito kawu bala yako zo da Sauri Wayar Umar ya mikamai Shiko yakoma baya yana Fadin"Abbah ka gane wannan dake tsaye..? Maimartaba dake tsaye, yayi Turus yana bin Fuskar kawu da kallo,wanda ke tsaye shima yana Bin Fuskar maimartaba da kallo,Kawu bala yakurama Abba ido yana kallonsa yaji hawaye sun kawomai komai Shekaru da dadewa bazai manta wannan Fuskarka ba,jikinsa na Rawa ya daga hannu yana Shafa Fuskar maimartaba yana Fadin"Abdul...Na...Naseer..."Bakinsa na Rawa Maimartaba dake tsaye,matansa da Mahaifiyarsa sun zagayesa tun sadda sukaji Umar na Fadin Ya gane wannan? Maimartaba ya Fashe da kuka yana Fadin" *BALA*.
..."ya fada hawaye suna zubomai Kawu ma kukan yake yana Fadin"Abdulnaseer dama kana raye ina ka Shigeni Muda mallam mun nemeka har mun gaji.."Maimartaba yace,"lbri ne mai Tsawo bala,mubar wannan sai nazo zakuji komai ammh yanzu ina Suwaiba don Allah karkacemin Suwaiba ta rasu.? yafada cikin Rawan murya Mirmishi kawu yayi yana Fadin"Suwaiba bata mutu ba,tana nan da Ranta ammh yanzu bata kusa tana gombe tana zaune..." Maimartaba ya maimata"gombe...? gyada kai Kawu yayi yana Fadin"lbrin yana Tsawo bazai yuyu ta waya ba.."Maimartaba yace"Hakane,ammh don Allah bala ka Fadamin gaskiya da gaskene,bayan Tafiyata Suwaiba ta haihu,a mafarkina ina ganinta da da,kuma hakan yanunamin ina da nasaba da Abunda Allah ke nunamin..."Kawu baiyi mgana ba,illah jawo hannun Aliyu dayayi wanda ke gefe yana Tsiyayan hawayen Farincikin jin muryan wani dattijo da sunan mahaifinsa,yana jawosa ya tsayar dashi kusa da Umar,Maimartaba da Sauran su Ummah suka daskare atsaye ganin wani mai kama da Umar sak,da badon Umar din na tsaye awajen ba tabbas zasu karyata suje umar ne,Aliyu ya dago kanshi yana kallon Fuskar Mahaifinsa wanda Manyatane kadai ta bambata danashi,ammh hatta tsawon da gashin kansa duka dayane,harda hancinsa da Shape din Fuskarsa,Sai fuskar kakarsa wacce ta haifi maimartaba itama kamar tashi Fuskar,sai Fuskar kannenshi mata wadanda yadda kikasn dukkansu sun Fita daga mahaifa daya,Kallonsu yake wani hajijiya na yawo dashi Don gani yake kamar ba gaske ba,Zafira da Safaratu da mamaki ya kamasu suka daka tsalle suna nuna Aliyu suna Fadin"La Abbah kalli mai kama damu ku kalli mai kama da Yaya yarima...? Maimartaba da gaban Rigansa ya jike da kwallah ya daga hannu ya shafa Fuskar Aliyu ta jikin wayar yana Fadib" yanzu Suwaiba ita ta haifamin kai da gaske...? yafada yana sakin yar dariya Aliyu ya gyada kai shima yana mika hannu kamar zai tabo mahaifinsa nasa yace"Ab...Abb...Abbbah....!!!Yafada muryansa na hadewa Jabir dake gefe yana leke shima yana kwallar,Aliyu saboda murna baisan sadda ya fada jikinsa kawu ba yana kuka kamar karamin yaro,don saboda yadda Farinciki yayimai yawa ji yake kamar zai iya kashe rai saboda yadda yakejin kansa,Umar dake hawaye ya karbi wayar yana Fadin"Abbah Ashe nima ina da Dan"uwa Shima Soja ne Shugaba nane,Sunansa * CAPTAIN ALIYU ABDULNASEER TAMBARI BUZU*.." Ihu su Zafira suka saka murna sun samu wani dan",uwa Ummah kuwa mai babban daki,amsan wayar tayi tana Fadin"Allah Shine mai hikima Umar Ashe dalilin zuwanka Garin kenan,tabomin sabon megidana nakara ganinshi don yanzu bana yayinka.."Tafada tana dariya Aliyu dayaji haka ya dago yana kallonta yadda take dariya yasa ya karbi wayar yana Fadin"Nima bani so akai kasuwa..",Dariya su zafira su saka sanya,maimarbata na tsaye Shima yana dariyan.

    Gimbiya Fasilatu,kuwa daskarewa tayi lalle Tsugunne bata kare ba tana Tunanin cewa itace Tauraruwa awajen sarki itace ta haifan mai magaji,ashe akwai wani boyayyen Sirri da basu sani ba,ashe akwai wata mace wacce take da babban mtsayi azuciyar Maimartaba,uwa uba ga kuma bayyanar wani da'n gareshi wanda ya D'arama Umar akomai,Turkashi,Itako Gimbiya Razeenah murna tacika cikinta ko bazan yanzu bakin gimbiya Fasilatu b zai mutu,kullum cikin Fariya take itace uwar magajin Sarki wato Yarima Umar,Saboda takaramata haushi itama Shigewa tayi cikinsu Ummah suna ta hira da Umar da Aliyu harda Jabir wanda Aliyu ya nunama maimartaba amtsayin Amini garesa,Nan fa akaita hira ana dariya su Zafira murna kamar ta kashesu sun samu sabon yaya,Duk rashin mganar Aliyu sai gashi ya zage yana Surutu da kannensa kamar bashi ba.

  Jabir ne aka kira akace su Fito Atisayen harbi,Dalilin daya sanya Aliyu cewa"Ok kiddo's matas,mommy,kubari mudawo yau kwana zamuyi muna mgana,yanzu zamu tafi wajen atisayen harbi ne,"Maimartaba ya karbi wayar yana Fadin"Kubama Bala wayar,Tundazu kun hanamu mgana.."dariya sukayi kan su mikama kawu bala wayar nan Maimartaba ke Shaidamai cewa!Gobe in Allah ya yarda dashi da duka iyalansa zasu sauka a gombe,.." baki Kawu ya washe yana Fadin"Masha Allahu.."Maimartaba yace"ina neman alfarman kada ku sanar da Suwaiba komai,kawai  sai dai taganni" gyada kai Kawu yayi yana Fadin"Hakan ma yayi nima gobe zamu hadu a gombe duka nida iyalaina.."jinjina kai maimartaba yayi yana fadin"Alhamdulillah Allah Abun godiya...",Kafin suyi sallama su yanke kiran Babu bukatar wani bayani su Aliyun sunji komai basu bata lokaci ba sukayi sallama da kawu Suka Fito,suka wuce wajen atisayen harbi,shikuma ya juya zuwa gida Shida tawagansu Don lbrin dake cikinsa bazai iya komawa office ba.

Shiko maimartaba suna yanke wayar ya Rumgume Ummah yana murna su Zafirama suka Rumgumeshi sunamai murna hakama gimbiya Razeenah ke nuna murnanta afili,Gimbiya Fasilatu dai na gefe tana yaken dole ranta duk ba dadi,itako Gimbiya Razeenah tana kallonta Farinciki yacika ranta,Maimartaba ya dago yana Fadin"Akiramin sarkin gida,..."Yafada da dan karfi,nan da nan fadawan dake waje suka isar da sakon sarki kan kace kwabo sai ga sarkin gida ya iso,Falon Shashen maimartaba ya tsaya inda maimartaba ya Fito ya sameshi da kafarsa Jikinsa da kuzari yana mai nuna murnansa Sarkin gida ya mike yana fadin",Allah Taimaki sarkin Agadez mai mulkan Masarautarmu Ta tambari buzu Allah dai yakarama Sarki lafiya,Gani kiran Adalin sarki ba"a yimishi jinkiri...",Dariya maimartaba yayi yana zama kafin yace"Sarkin gida katashi yanzu katafi kakira waya zuwa Nageria,inaso in sanar dakai kakira Waya zuwa Masarautar garin gombe ka sanar cewa zan zo kasarsa dakuma jaharsa agobe,Ammh kabari sai waziri yazo munyi mgana dashi ashiryamana jirgin masaurata in yagamaka lokacin dazamu isa sai kakira wayar..",Jinjina kai Sarki gida yayi yana Fadin"Allah karamaka yawan Rai,angama...",Yatashi da hanzari zai Fice sarki yace"Ka fadama Waziri yazo yanzu inason ganinshi..." Sadda kai Sarkin gida yayi yana fadin "Yanzu kuwa Adalin sarki.." yafada yana Hucewa.

  
*JANAFTY*

You are reading the story above: TeenFic.Net